in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta kara kashe kudade a bangaren ilimi a shekarar 2018
2019-05-02 15:15:23 cri
Wani sabon rahoto da ma'aikatar ilimi ta kasar Sin ta fitar, ya bayyana cewa, a shekarar 2018 da ta gabata, kasar ta kara yawan kudaden da take kashewa a bangaren Ilimi, inda ta kashe sama da Yuan triliyan 4.6, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 685 a bangaren na Ilimi a fadin kasar, karuwar kaso 8.39 cikin 100 kan shekarar da ta gabata ce.

Rahoton ya ce, kasafin kudin da gwamnati ta warewa a bangaren Ilimi, ya kai sama da Yuan triliyan 3.6, adadin da ya karu da kaso 8.13 cikin 100 kan na shekarar da ta gabata.

Bugu da kari, rahoton ya nuna cewa, kusan rabin kudaden da aka kashe ya karkata ne ga bangaren samar da ilimi tilas, sai bangaren ilimin manyan makarantu, wanda ya kasance na biyu mafi girma tsakanin dukkan sassan Ilimin kasar. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China