in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatar ilimi ta kasar Sin ta bukaci a mara baya ga yaki da talauci
2019-04-26 10:57:48 cri
Ministan ilimi na kasar Sin, Chen Baosheng, ya yi kira da a kara himmantuwa wajen inganta ilimi domin taimakawa yakin da gwamnatin kasar ke da fatara.

Chen Baosheng, ya bayyana haka ne a wani taro da aka yi kan shirye shiryen rage fatara a bangaren ilimi, wanda ya gudana lardin Yunnan.

Ministan ya yi kira ga jami'o'i da cibiyoyin ilimi dake cikin shirye-shiryen, su mayar da hankali kan manyan matsaloli, su kuma bullo da matakan da za su magance su, tare da yin aiki bisa kwarewa.

Ya ce ya kamata bayanai game da matakan tabbatar da samun ilimin da ya zama na dole na shekaru 9 da takaita yawan masu barin makaranta a yankuna masu fama da talauci da kuma yanayi da adadin yaran da suka isa zuwa makaranta a gidaje matalauta, su kasance bisa sanin cikakken yanayin da ake ciki.

Ya kuma bukaci a zabi jami'an da suka kware domin gudanar da shirye shiryen.

Har ila yau, ya ce ana bukatar karfafa sa ido domin tabbatar da samun sahihan sakamako daga shirye-shiryen. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China