in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi sharhi game da ficewar Amurka daga yarjejeniyar ATT
2019-04-30 19:50:27 cri
Kasar Sin ta bayyana fatan cewa, kasashen dake cikin yarjejeniyar cinikayyar makamai (ATT) za su kara yin abubuwan da suka dace, don karfafa matakan takaita makamai na duniya tare da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.

Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, shi ne ya bayyana hakan, bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da janyewar kasarsa daga yarjejeniyar cinikayyar makamai ta ATT a ranar 26 ga watan Afrilu, yarjejeniyar dake sanya ido kan cinikayyar makamai ta kasa da kasa da kandagarki da magance yin cinikayya ba bisa ka'ida ba, da canja akalar makamai, ta hanyar kafa ma'aunin ingancin kasa da kasa game da canzawa makamai matsuguni.

Geng ya ce, kasar Sin tana goyon bayan dalili da ma manufar kafa yarjejeniyar, kuma tana halartar tarukan da abin ya shafa a matsayin 'yar kallo. Bugu da kari, kasar Sin tana duba yiwuwar shiga yarjejeniyar. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China