in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta taimakawa kasashen Mozambique, Malawi da Zimbabwe da mahaukaciyar guguwa ta yiwa barna
2019-03-19 19:52:26 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya bayyana kudurin kasarsa na taimakawa kasashen Mozambique, da Malawi da Zimbabwe wadanda mahaukaciyar guguwa mai tafe da ruwan sama ta Idai ta yiwa mummunan barna.

Geng Shuang wanda ya bayyana hakan a Talatar nan yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, ya ce a shirye kasar Sin take ta taimakawa kasashen da wannan ifta'i ya shafa daidai karfinta kuma kamar yadda gwamnatocin kasashen uku suka bukata.

Ya ce, gwamnatin kasar Sin, tana jajantawa kasashen Mozambique da Malawi da Zimbabwe bisa ga asarar rayuka da dukiyoyin da mahaukaciyar guguwar ta haddasa, tana kuma mika ta'aziya ga iyalan wadanda suka mutu tare da fatan samun sauki cikin hanzari ga wadanda suka jikkata.

Kimanin mutane 84 ne aka ba da rahoton sun mutu a Mozambique, 56 a kasar Malawi sai kuma mutane 98 a kasar Zimbabwe.

Sai dai shugaba Filipe Nyusi na Mozambique ya bayyana a jiya Litinin cewa, yawan wadanda suka mutu a kasarsa zai haura 1,000. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China