Yayin ziyarar, jami'an diflomasiya daga kasashen Myanmar, da Aljetiya da Morocco, da Vietnam, da Hungary, da Greece, da Singapore gami da wata tawaga daga kungiyar kasashen Larabawa dake nan kasar Sin, sun ziyarci sassa daban-daban dake yankin, sun kuma tattauna sosai da mazauna wuraren.
Jami'an sun bayyana cewa, sun ji dadin yadda mazauna yankin ke mu'amala da jama'a da yadda kabilu daban-daban dake yankin suka hada kansu da ma irin nasarorin da yankin ya samu a fannin inganta rayuwar jama'a.
A jawabinsa shugaban tawagar kungiyar kasashen Larabawa dake nan kasar Sin Mahmoud Hassan Elamin, ya ce, ziyarar ta ba su damar kara fahimtar yankin, yana mai cewa, ci gaban yankin, zai baiwa kowa da kawo damar amfana dai-dai gwargwado. (Ibrahim Yaya)