in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta damu da bukatun fararen hula yayin da ake tsaka da luguden wuta a Tripoli
2019-04-30 10:15:59 cri

Shirin wanzar da zaman lafiya na MDD a Libya, ya bayyana fargabar cewa, ciyar da fararen hula da suka makale saboda yaki a sassan birnin Tripoli, na kara zama matsala mai tsanani, duk da kiran da ake yi na kare fararen hula daga hare-haren.

Kakakin MDD Stephane Dujarric, ya ce shirin ya damu da yadda isar abinci ga fararen hula da 'yan gudun hijira da masu kaura dake yankunan da ake rikici ke kara zama babbar barazana.

Ya ce suna ci gaba da kira da a ba jami'an agaji damar kai dauki ga bukatun al'umman da fadan ya shafa, ba tare da wani sharadi ba.

Da yake bada misali daga rahotannin kungiyoyin lafiya, ya ce wani yaro da hare-haren ta sama ya rutsa da shi ya mutu. Ya ce tun bayan barkewar rikicin a farkon watan nan, an tabbatar da jimilar fararen hula 96 da hare-haren suka shafa, ciki har da 22 da suka mutu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China