in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Libya za ta sake bude rijiyar hakar man fetur mafi girma ta kasar
2019-02-27 10:30:27 cri
Gwamnatin Libya da MDD ke marawa baya, ta sanar da cewa za ta bude rijiyar hakar man fetur ta Sharara, wadda ita ce mafi girma a kasar, bayan ayyana dakatar da aiki a wajen.

A wani bangare na ziyararsa a Hadaddiya Daular Larabawa, Firaministan gwamnatin Fayez Serraj, ya gana da shugaban kamfanin mai na kasar NOC, Mustafa Sanalla a birnin Abu Dhabi, inda ya amince kamfanin ya dauki matakan tsaron da suka dace a wajen hakar man.

A watan Disamban bara ne kamfanin mai na kasar NOC ya sanar da dakatar da yarjejeniyar aiki a rijiyar Sharara, biyo bayan tilasta musu rufewa da wata kungiyar masu dauke da makamai ta yi.

A baya-bayan nan ne rundunar sojin dake da mazauni a gabashin kasar, ta kwace iko da rijiyar, inda ta yi kira ga kamfanin NOC ya dage batun dakatar da aikin. Sai dai kamfanin, ya bukaci jami'an tsaro su bar wajen kafin a sake budewa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China