in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta gina tashar binciken kimiya a yankin kudancin duniyar wata
2019-04-24 14:11:44 cri
Shugaban hukumar binciken sararin samaniya ta kasar Sin Zhang Kejian, ya bayyana cewa, kasarsa na shirin gina wata cibiyar binciken kimiya a yankin kudancin duniyar wata, inda za ta gudanar da binciken sararin samaniya na kimanin shekaru goma.

Jami'in ya bayyana hakan ne yayin bikin bude ranar nazarin sararin samaniyar kasar Sin da ya gudana a Changsha, babban birnin lardin Hunan dake tsakiyar kasar Sin.

Zhang ya kuma bayyana cewa, kasar Sin za ta harba tauraron dan-Adam na Change-5, don dawo da samfurorin da ya tattaro zuwa doron duniyarmu a karshen shekarar 2019. Haka kuma kasar ta Sin na harba wani tauraron dan-Adam na farko don gudanar da bincike a duniyar Mars a shekarar 2020. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China