in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumomin agaji na kokarin taimakawa 'yan kasar Mozambique miliyan 1.8 da guguwar Idai ta shafa
2019-04-24 10:08:41 cri
Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD (UNHCR) a takaice , ta ce, kimanin mutane miliyan 1.8 ne ke bukatar agajin jin kai a kasar Mozambique, yayin da a hannu guda hukumomin agaji ke fuskantar manyan kalubale, sakamakon karancin kudi da lalacewar kayayyakin more rayuwa.

Mai magana da yawun hukumar ta UNHCR Babar Baloch, ya shaidawa taron manema labarai cewa, gwamnatin Mozambique da hukumar ta UNHCR da sauran abokan hulda, sun fara mayar da iyalan da mahaukaciyar guguwar Idai ta raba da muhallansu zuwa wasu yankunan dake kusa da gidajensu na asali.

Baloch ya ce, suna fatan, nan da kwanaki 10 masu zuwa, kimanin mutane 700 za su bar sansanonin wucin gadi da suka hada da makarantu, dakunan taron jama'a, da dakunan karatu da sauran gine-gine da suka shafe sama da wata guda suka zaune.

A tsakiyar watan Maris din da ya gabata ne dai, mahaukaciyar guguwar Idai mai tafe ta ruwan sama, ta shafi kasashe kudancin Afirka da suka hada da Mozambique da Malawai, da kuma Zimbabwe. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China