in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadan Sin ya jaddada bukatar ci gaba da wanzar da zaman lafiya a Darfur ta hanyar siyasa
2019-04-18 16:36:31 cri
Mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Wu Haitao, ya jaddada bukatar ci gaba da wanzar da zaman lafiya a yankin Darfur na kasar Sudan ta hanyar siyasa. Wu Haitao ya bayyana hakan ne, yayin zaman kwamitin tsaron MDD game da halin da ake ciki a Sudan da yankin Darfur na kasar.

Wu ya ce a halin da ake ciki, yankin Darfur yana da matukar muhimmanci ga wanzuwar zaman lafiya a Sudan, kuma akwai bukatar daga matsayinsa daga yanayin wanzar da zaman lafiya zuwa sake gina kyakkyawan yanayi na kwanciyar hankali.

Ya ce ya kamata kasashen duniya su ci gaba da aiwatar da matakan siyasa, da na wanzar da zaman lafiya, domin cimma burin daidaita al'amura sannu a hankali, har a kai ga mika mulki ga farar hula lami lafiya ba tare da amfani da karfin soja a kasar ta Sudan ba. Kana a yi hadin gwiwar wanzar da zaman lafiya da tsaro a yankin Darfur mai fuskantar ayyukan 'yan aware. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China