Ana sa ran ziyarar za ta inganta musayar dabaru tsakanin hafsoshin na Afrika da takwarorinsu na kasar Sin, da zurfafa abota tsakanin rundunonin sojin Sin da Afrika da kuma karfafa hadin gwiwar bangarorin biyu a fannin tabbatar da tsaro da zaman lafiya.
Hafsoshin sojin na Afrika, za su kai ziyara kwalejoji da sansanoni da masana'antun rundunar sojin kasar Sin.
Za kuma su saurari lakca kan maudu'ai daban daban, ciki har da kawancen soji karkashin shawarar "Ziri Daya da Hanya Daya". (Fa'iza Mustapha)