Yau Jumma'a, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana cewa, ko wadanne irin sauye-sauyen za a samu a kasar Sudan, kasar Sin za ta ci gaba da kiyayewa, da kyautata huldar abota, da yin hadin gwiwa a tsakaninta da Sudan.
Kalaman na Lu Kang na zuwa ne, bayan da rundunar sojojin kasar ta Sudan, ta kifar da gwamnatin farar hulan kasar. (Tasallah Yuan)