in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani hari a arewacin Nijeriya ya yi sanadin mutuwar mutane 21
2019-04-10 09:56:45 cri

Rundunar 'yan sandan Nijeriya ta tabbatar da mutane 21 sun mutu a wani hari da wasu, da ba a san ko su waye ba, suka kai jihar Kaduna dake arewacin kasar.

Kakakin rundunar 'yan sandan jihar Kaduna Yakubu Sabo, ya shaidawa manema labarai cewa, wasu 'yan bindiga sun kai hare-hare kauyukan Ungwan Aku da Banono na yankin karamar hukumar Kajuru ta jihar.

Yakubu Sabo ya ce an gano gawawwaki 21, sannan wasu mutane 3 sun ji rauni, baya ga kone gidaje 10 da maharan suka yi.

Duk da barnar da suka yi a kauyukan, 'yan bindigan sun kuma sace shanu 50 yayin harin.

Kakakin 'yan sandan ya ce 'yan bindigar sun kai farmaki kauyukan ne a kan babura.

Ya kara da cewa, tuni aka kaddamar da bincike kan lamarin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China