Wata arangama tsakanin 'yan kungiyar sintiri da wasu 'yan bindiga a jihar Katsina dake arewa maso yammacin Nijeriya, ta yi sanadin mutuwar mutane 7.
Rundunar 'yan sanda jihar ta ce ta gano gawawwaki 7 jiya da safe, biyo bayan arangamar da aka yi ranar Litinin, wadanda ake tsammanin na mambobin kungiyar sintiri ne, na kauyen Tsamiyar Jino dake karamar hukumar Kankara ta jihar.
Kakakin rundunar Gambo Isa, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua na kasar Sin cewa, da jin labarin wasu 'yan bindiga na taruwa a wani daji dake kusa da kauyen, sai 'yan sintirin suka kai musu farmaki ba tare da tuntubar rundunar 'yan sandan ba.
A cewar mazauna kauyen, 'yan bindigan sun shafe wani lokaci suna addabar yankin. (Fa'iza Mustapha)