in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Nijeriya ta dakatar da ayyukan hakar ma'adinai a jihar Zamfara
2019-04-08 14:04:15 cri
Gwamnatin Nijeriya ta dakatar da duk wani nau'i na hakar ma'adinai a jihar Zamfara dake arewa maso yammacin kasar.

Babban Sufeton 'yan sandan kasar Muhammad Adamu, ya bayyanawa manema labarai jiya a Abuja cewa, gwamnatin ta kuma umarci dukkan 'yan kasashen waje dake ayyukan hakar ma'adinai su bar yankin cikin sa'o'i 48.

Ya ce umarnin wani bangare ne na matakan dakile ayyukan bata gari a jihar.

A cewar Babban Sufeton, dakatarwar ta biyo bayan rahotannin sirri da aka samu cewa, akwai alaka mai karfi tsakanin ayyukan bata garin da masu hakar ma'adinai bisa haramtacciyar hanya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China