Samun sabbin rahotannin na baya bayan nan ya tabbatar da jimillar rahotannin bullar cutar 526 daga cikin adadin da ake zargi na kimanin 2,034 tun daga watan Janairu a jahohin kasar 21, Chikwe Ihekweazu, babban jami'in hukumar hana yaduwar cutuka ta Najeriya (NCDC) shi ne ya bayyana hakan a Abuja, babban birnin Najeriyar.
Ya shedawa manema labarai cewa, adadin mutane da suka mutu sun kai 121 tun bayan barkewar annobar cutar.
Ihekweazu ya kara da cewa akwai wasu jami'an kiwon lafiya cikin wadanda lamarin ya rutsa da su a jihar Filato dake shiyyar tsakiyar Najeriya, inda kawo yanzu aka samu ma'aikatan jiyya 17 da cutar ta shafa a jahohi 7 na kasar tun bayan barkewar cutar.
Shugaban hukumar ta NCDC ya tabbatar da cewa, manyan abokan aikin hukumar na kasa dake yaki da cutar ta Lassa, da manyan cibiyoyin ba da agajin gaggawa za su ci gaba da yin aiki tare domin dakile cutar a dukkanin matakai. (Ahmad Fagam)