Kakakin rundunar Ibikunke Daramola, wanda ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja, ya ce a ranar Lahadi ne 'yan bindigan suka farwa kauyukan Hayin Mahe da Hayin Kanawa dake Gusau, babban birnin jihar, inda ya ce da yawa daga cikin maharan sun tsere cikin daji da raunukan harbi.
Ibikunle Daramola, ya ce yayin harin, an sace wasu mazauna kauyukan, ciki har da mata 2 da yaro guda. Sai dai kuma jami'an da suka bi sawun maharan da suka tsere, sun yi nasarar ceto mutanen bayan sun yi bata kashi da su.
A cewarsa, daukin gaggawa da jami'an sun ka kai ya biyo bayan bayannan sirrin da suka samu game da ayyukan wasu 'yan bindiga a yankin. (Fa'iza Mustapha)