in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNMAS: Mutane 565 ne suka rasu sakamakon ababen fashewa da mayakan Boko Haram ke bunnewa a 2018
2019-04-05 15:59:22 cri
Wani rahoton da hukumar MDD mai lura da dakile yaduwar ababen fashewa ta UNMAS ta fitar ya nuna cewa, a shekarar 2018 da ta gabata, yawan mutanen da suka rasu, sakamakon taka ababen fashewa da mayakan kungiyar Boko Haram ke bunnewa a yankunan arewa maso gabashin Najeriya ya kai mutum 565.

Da yake karin haske game da rahoton, yayin wani gangami na bikin ranar kasa da kasa ta wayar da kai, da inganta ayyukan kau da ababen fashewa da aka gudanar a birnin Maiduguri, fadar mulkin jihar Borno, babban jami'in tsare tsare na hukumar ta UNMAS Lionel Pechera, ya ce ababen fashewa da ake bunnewa na zama wani babban kalubale ga manoma, wanda kuma hakan ke kara ta'azzara yanayin karancin abinci a sassan arewa maso gabashin Najeriya.

Jami'in ya kara da cewa, wasu daga sansanonin tsugunar da 'yan gudun hijira na cikin wurare dake dauke da irin wadannan ababen fashewa da ake bunnewa, wadanda a lokuta da dama ke raunata, ko ma hallaka fararen hula.

Lionel Pechera ya kara da cewa, wayar da kan al'umma, da tallafawa wajen aikin kawar da irin wadannan ababen fashewa daga maboyar su, muhimmin mataki ne na kare rayuka da dukiyoyin al'umma, tare kuma da samar da dama ta komawar al'ummun da suka tserewa gidajen su zuwa yankunan su.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China