in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta tabbatar da kashe mayakan Boko Haram 55 a aikin sintirin dakarun hadin gwiwa
2019-03-15 10:31:59 cri
Kimanin mayakan Boko Haram 55 aka hallaka cikin kwanakin biyun da suka gabata bayan kaddamar da aikin sintirin hadin gwiwar dakarun kasashen Najeriya, Chadi, Kamaru, Benin da Nijer, rundunar sojojin Najeriya ne ta tabbatar da hakan a jiya Alhamis.

Dakarun tsaron hadin gwiwar, a yayin da suke gudanar da ayyukansu, sun gano wasu tarin makamai a wani waje dake tafkin Chadi, Timothy Antigha, jami'in rundunar sojojin Najeriya wanda kuma shine babban jami'i mai magana da yawun rundunar tsaron hadin gwiwar ya bayyana hakan.

An kaddamar da aikin farautar mayakan 'yan ta'addan ne a yankin Tumbun Rego, wanda shine babbar maboyar mayakan 'yan ta'addan dake tafkin Chadi, inji Antigha

Tumbun Rego, wani sanannen tsibiri ne a tafkin Chadi, wanda aka yi amannan shine wajen da manyan kwamandojin kungiyar Boko Haram ke samun mafaka.

An gano gawarwakin mayakan 'yan ta'addan 33 a yankin Tumbun Rego, yayin da ragowar 22 aka hallakasu a wani harin na daban wanda dakarun hadin gwiwa suka kaddamar a yankin Arege dake kan iyakar Najeriya, wanda shima wata babbar maboya ce ta mayakan Boko Haram dake kusa da tafkin Chadi.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China