Yankin Diffa yana kan iyakar Nijer da Nijeriya, kuma dakarun Boko Haram sun sha kai hare-hare wannan yanki a cikin 'yan shekarun baya, wadanda suka yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama. A watan Yulin shekarar 2016 ne, sojojin tsaron dangin kasashen Nijeriya da Kamaru da Nijer da kuma Chadi sun fara yakar 'yan Boko Haram. (Lubabatu)