in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta bukaci a dauki kwararan matakai don rage hasarar amfanin gona da ake samu lokacin kaka
2019-04-02 10:26:23 cri
Kungiyar tarayyar Afrika (AU) ta bukaci kasashen Afrika da hukumomin da abin ya shafa da su sa kaimi wajen daukar matakan rage hasarar dunbun amfanin gona da ake samu a lokacin kaka bayan an kammala girbin amfanin gonar domin magance matsalar karancin abinci dake addabar nahiyar.

Afrika ta kasance nahiyar da aka fi fama da kamfar abinci a duniya, yayin da kusan ake samun mutum guda daga cikin mutane 4 dake fama da karancin abinci mai gina jiki, in ji kungiyar ta AU.

A cewar kungiyar ta Afrika, a shekaru masu yawa, mafi yawan kasashen Afrika suna mayar da hankali ne wajen kara samar da abinci, amma a cewar AU, yawan abincin da ake tafka hasara a duk shekara ya zarta hatsin da ake shigowa da shi daga kasashen ketare zuwa Afrikar.

Wannan matsalar hasarar abincin da ake samu tana matukar haddasa karancin abinci kuma tana da mummunan tasiri ga muhalli ta hanyar lalata filaye da ruwa, da kayayyakin aikin gona da makamashin da ake amfani da shi wajen samar da abincin, in ji kungiyar ta AU. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China