in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta gabatar da tayin gudanar da taron wanzar da sulhu a Libya
2019-04-02 10:08:53 cri

Shugaban hukumar zartaswar kungiyar tarayyar Afirka ta AU Moussa Faki, ya gabatar da tayin gudanar da taron wanzar da sulhu a Libya, yayin wata ganawa da ya yi da firaministan kasar mai samun goyon bayan MDD Fayez Serraj.

Moussa Faki ya gabatar da shawarar ne a jiya Litinin a birnin Tripoli, fadar mulkin kasar ta Libya, yana mai cewa al'ummar kasar ne kadai za su iya yanke hukunci, game da batutuwan da suka shafi siyasar kasar. Ya kuma soki duk wani mataki na tsoma hannu wasu sassa na waje, cikin batun siyasar kasar, matakin da a cewarsa na kara dagula al'amuran kasar.

Wata sanarwa da ofishin Mr. Faki ya fitar, ta ce firaministan na Libya ya amince da wannan shawara, yana mai fatan za a gudanar da taron sulhun karkashin jagorancin MDD. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China