in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi gargadin yiwuwar barkewar cutar kwalara a arewa maso gabashin Najeriya
2019-04-02 09:15:11 cri
Wata kungiyar bada agaji ta kasa da kasa ta yi gargadin cewa karancin kayayyakin tsabtar muhalli a sansanonin 'yan gudun hijira mai fama da yawan cinkoson jama'a zai iya haddasa yiwuwar barkewar cutar kwalara a shiyyar arewa maso gabashin Najeriya.

Cikin wata sanarwar da ta aikewa kamfanin dillancin labarai na Xinhua a ranar Litinin, kungiyar Norwegian Refugee Council (NRC) ta bukaci a dauki matakan dakile barazanar da yankin na arewa maso gabashin Najeriya ke fuskanta, yankin dake karbar bakuncin dubban mutane wadanda suka kauracewa gidajensu a sakamakon yawan hare-haren mayakan 'yan ta'adda na Boko Haram.

A cewar wani rahoton cibiyar dakile yaduwar cututtuka ta Najeriya, a shekarar 2018, an samu rahoton mutane 50,719 daga jihohin kasar 30 da ake zaton sun kamu da cutar ta kwarala.

NRC ta yi gargadin cewa, mai yiwuwa ne a samu saurin bazuwar cutar a wannan shekarar kasancewar ana samun karuwar mutane dake kauracewa gidajensu lamarin da ke haifar da cunkoson jama'a a sansanonin. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China