in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya bayyana rashin jin dadi game da ruftawar ginin makaranta a Legas
2019-03-14 10:09:27 cri

 

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana rashin jin dadi sakamakon ruftawar wani bene mai hawa uku na wata makarantar firamare a yankin Ita-Faji dake jahar Legas, inda ya yi sanadiyyar kashe rayuka, musamman kananan yara.

A wata sanarwa da aka fitar a Abuja, shugaba Buhari ya jajantawa iyayen yara da dangin wadanda hadarin ya rutsa da su kana ya yi fatan samun sauki cikin gaggawa ga wadanda suka samu raunuka.

Shugaban kasar ya bukaci gwamnatin jahar Legas, cibiyar kasuwancin Najeriyar, da ta dauki dukkan matakan da suka dace domin kaucewa afkuwar irin hakan a nan gaba.

Wani jami'in aikin ceto a yankin ya bayyana cewa, an samu nasarar zakulo gawarwakin mutane 9 daga cikin burabuzan ginin kana akwai wasu mutanen da dama da ginin ya danne su, wanda ya hada da ginin makaranta, da shaguna da kuma wasu gidajen kwanan jama'a, wadanda ginin ya afka musu da safiyar ranar Laraba a birnin Legas.

Wani jami'i ya fada wa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, kimanin yara 'yan makaranta 172 ne aka yi wa rejista a makarantar, kuma kawo yanzu an ceto yara 50.

Har yanzu ba'a tantance musabbabin ruftawar ginin ba. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China