in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Barkewar cutar kyanda ta yi sanadin mutuwar yara 13 a arewacin Nijeriya
2019-03-23 15:47:46 cri
Yara 13 ne aka tabbatar sun mutu sanadiyyar barkewar cutar kyanda a jihar Borno dake arewa masu gabashin Nijeriya.

Wata sanarwa daga hukumar kula da lafiya a matakin farko na jihar da ta shiga hannun kamfanin dillancin labarai na Xinhua, ta ce cutar da ake samu daga ruwan sha, ya bazu ne a fadin yankunan kananan hukumomi 25 na jihar.

Hukumar ta kara da cewa, Cutar, wadda ke ja gaba wajen haifar da asarar rayuka a kasashe masu tasowa kamar Nijeriya, na kara karuwa a jihar Borno, inda yara 4,693 suka kamu kawo yanzu.

A cewar daraktan cibiyar takaita yaduwar cutuka ta jihar, Babagana Abiso, yanzu haka, ana kokarin dakile bazuwar cutar.

Kyanda cuta ce da ake samu daga hanyar kwayoyin cuta a tsakanin yara. Kuma ya kan yi tsanani har ma ya kai ga asarar rai a tsakanin yara kananan.

Jami'in ya ce, asusun kula da yara na MDD UNICEF da hukumar lafiya ta duniya WHO, za su samar da taimakon da ake bukata yayin aikin riga kafi na kwanaki 10. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China