Kakakin rundunar 'yan sandan jihar Yakubu Sabo, wanda ya bayyana haka ga manema labarai, ya ce tuni jami'an tsaro suka fara bincike a kauyen da nufin ceto limamin mai suna John Bako Shekwolo da kuma cafke wadanda suka sace shi.
Yakubu Sabo ya ce an sace John Shekwolo ne ranar Litinin da da daddare. (Fa'iza Mustapha)