in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala taron gamayyar kasashen Larabawa tare da bukatar kafa kasar Palastinu
2019-04-01 12:01:20 cri
Da yammacin ranar Lahadi aka kammala taron kolin gamayyar kasashen Larabawa (AL) karo na 30, tare da yin kiran a tabbatar da kafa 'yantacciyar kasar Palastinu da kuma nuna goyon bayan warware rikicin dake tsakanin bangarorin biyu wato Israeli-Palestinu.

"Ba za'a taba amincewa da ci gaba da yanayin da ake ciki a halin yanzu ba wanda ya mayar da yankin kasashen Larabawa a matsayin yanki mai fuskantar tashe-tashen hankula da rikice-rikice wanda ke barzana ga tsaro, zaman lafiyar, da kuma ci gaban kasashenmu," in ji ministan harkokin wajen kasar Tunisia Khemaies Jhinaoui, yayin da yake fitar da sanarwar karshen bayan kammala taron kolin.

Game da batun kasar Syria kuwa, wanda aka yi matukar tattaunawa kansa a lokacin taron kolin, duk da cewa shugaban kasar ta Syrian bai halarci taron ba, sanarwar karshen ta tabbatar da cewa, shugabannin kasashen Larabawa za su yi amfani da matakan siyasa domin kawo karshen rikicin Syria da kuma magance matsanancin halin da al'ummar kasar ke ciki da tabbatar musu da burin da suke da shi na ci gaba da rayuwa cikin yanayin zaman lafiya da tsaro, kana da tabbatar da hadin kan kasar Syriar da ikon da kasar ke da shi na gudanar da yankunanta bisa 'yancin kai.

Sanarwar karshen ta amince da yankin nan na Golan Heights a matsayin wani bangare mallakin kasar Syria, bisa ga tsarin dokokin kasa da kasa, da yarjejeniyar kwamitin sulhun MDD. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China