in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masar da Jordan sun yi kira da a kare hakkin Palasdinawa
2018-04-02 14:07:11 cri
Ministocin harkokin wajen kasar Masar da Jordan sun gudanar da taron manema labaru na hadin gwiwa a birnin Alkahira a ranar 1 ga wannan wata, inda suka yi Allah wadai da sojojin kasar Isra'ila, bisa harba wasu masu zanga-zanga Palasdinawa har lahira a zirin Gaza a kwanakin baya. Kasashen sun kuma yi kira ga kasa da kasa da su sauke nauyin dake wuyan su na kare hakkin Palesdinawa.

Ministan harkokin wajen kasar Masar Sameh Shoukry, ya bayyana a gun taron manema labarun cewa, ya kamata kasa da kasa su dauki alhakin kare hakkin Palesdinawa, da sa kaimi ga shimfida zaman lafiya a yankin. Ya ce, kasar Masar za ta ci gaba da yin kira da a tabbatar da hakki da moriyar Palesdinawa bisa kudurorin kasa da kasa masu nasaba da hakan.

A nasa bangaren kuwa, ministan harkokin wajen kasar Jordan Ayman Safadi ya bayyana cewa, ya kamata a warware batun Palesdinu ta hanyar siyasa, da baiwa Palesdinawa damar farfado da imanin kiyaye hakkinsu. Ya ce kasarsa ta yi Allah wadai da kasar Isra'ila, bisa illata yanayin shimfida zaman lafiya, da shirin kasashen biyu kan batun Palesdinu da Isra'ila.

Hazakalika kuma, ministocin biyu sun kalubalanci kasar Amurka, da ta dauki matakai cikin hanzari don warware batun Palesdinu da Isra'ila ta hanyar siyasa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China