in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a sassauta halin da ake ciki tsakanin Palesdinu da Isra'ila
2018-06-02 15:56:39 cri
Zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Ma Zhaoxu, ya bayyanawa kwamitin sulhu na MDD cewa, kasarsa na kira ga Isra'ila da Palesdinu musamman Isra'ila, ta kwantar da hankali, da sa kaimi ga sassauta halin da ake ciki tsakanin kasashen biyu, domin magance asarar rayuka da jikkatar mutane.

Kwamitin sulhun ya kada kuri'a game da kudurori biyu kan batun Palesdinu, wadanda kasar Kuwait da Amurka suka tsara, amma kuma ba a zartas da su ba.

Ma ya bayyana cewa, kudurin da kasar Kuwait ta gabatar, ya shaida halin da ake ciki, wanda ya taimaka wajen tabbatar da tsaron fararen hula na Palesdinu, da sassauta halin da ake ciki tsakanin Isra'ila da Palesdinu. Ya ce kasar Sin ta yabawa Kuwait bisa kokarinta na neman cimma daidaito a tsakanin bangarori daban daban, a don haka Sin ta amince da kudurin da Kuwait din ta gabatar.

Ma ya kara da cewa, ya kamata kwamitin sulhu na MDD da kasa da kasa su dauki matakan biyan bukatun da suka dace na Palesdinu da Larabawa, da sa kaimi ga yin shawarwarin shimfida zaman lafiya a tsakanin Palesdinu da Isra'ila cikin hanzari, da cimma burin kafa kasashen biyu don samun zaman lafiya a tsakaninsu.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China