in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Zimbabwe zai yi rangadin yankunan da guguwar Idai ta aukawa tare da 'yan jam'iyyar adawa
2019-04-01 10:27:43 cri
A wannan mako ne Shugaban kasar Zimbabwe, Emmerson Mnangagwa, zai yi rangadin yankunan kasar da guguwar Idai ta shafa tare da wasu wakilai 17 na jam'iyyar adawa dake cikin shirin tattauna batutuwan kasa, wadda ke da nufin warware matsalolin tattalin arziki da siyasa na kasar.

Sakataren yada labarai na kasar Nick Mangwana, wanda ya wallafa batun a shafinsa na Tweeter a jiya Lahadi, ya ce Shugaba Mnangagwa wanda a baya ya kai ziyara lardin Manicaland, zai kara ziyartar lardin da sauran yankunan da iftila'in ya shafa a larduna 3 na Mashonaland ta gabas da Masvingo da kuma Midlands.

Sakataren ya kara da cewa, abu ne mai kyau shugabanni su shiga cikin al'umma su kuma nazarci abubuwa da kansu.

Shirin tattauna batutuwan kasar ya kunshi 'yan takarar shugaban kasa na zaben 2018 da wasu daga cikin jami'an wasu jam'iyyun.

Emmerson Mnangagwa, shi ne wakilin Jam'iyyar ZANU PF mai mulki, sai dai babbar jam'iyyar adawa ta MDC dake karkashin Nelson Chamisa, ta yi watsi da shirin, tana mai zargin cewa shugaba Mnangagwa ba shi da gaskiya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China