in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in MDD ya nuna damuwa game da hasarar rayukan da mahaukaciyar guguwa ta haddasa a Zimbabwe
2019-03-18 09:49:36 cri

Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya bayyana damuwa game da hasarar rayukan da aka samu, da barnata dukiyoyi da kuma tilastawa mutane barin gidajensu a Zimbabwe a sakamakon mamakon ruwan sama da ambaliyar ruwa wanda mhaukaciyar guguwar Idai ta haddasa, kakakin babban sakataren ne ya bayyana a ranar Lahadi.

Guterres, ya aike da sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda ibtila'in ya rutsa da su da al'ummar kasar da gwamnatin kasar Zimbabwe, inji Stephane Dujarric, kakakin MDD.

Hukumar MDDr tace tana goyon bayan hukumomin kasar ta Zimbabwe kuma a shirye take tyi aiki tare dasu wajen samar da ayyukan jin kai da ake bukata wanda bala'in ya haddasa, inji sanarwar.

Mahaukaciyar guguwar ta Idai tayi sanadiyyar hallaka mutane 150 a kasashen Malawi, Mozambique da Zimbabwe, yayin da wasu daruruwan mutane suka bace.

Kakakin na mista Guterres ya gabatar da makamanciyar sanarwar ga kasashen Malawi da Mozambique a lokuta daban daban a ranakun Litinin da Juma'a.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China