Wani gini mai hawa uku na wata makarantar Firamare a jihar Lagos dake kudancin Najeriya ya rufta, ana kuma tsoron dalibai da dama sun makale a baraguzan ginin.
Rahotanni na cewa, akwai yiwuwar wasu daga daliban sun rasu, sakamakon wannan hadari da ya auku da safiyar yau Laraba.(Saminu Alhassan)