in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin Birtaniya ta kada kuri'ar neman tsawaita kudurin ficewar kasar daga EU
2019-03-15 11:15:45 cri

'Yan majalisar dokokin Birtaniya sun kada kuri'ar neman Tarayyar Turai EU ta jinkirta batun ficewar kasar daga kungiyar.

'Yan majalisar sun kada kuri'ar amincewa 412 a kan 202 da suka ki, inda aka samu bambancin kuri'u 210, da nufin neman amincewar EU na jinkirta ficewar kasar zuwa ranar 30 ga watan Yuni.

Sakamakon na nufin bukatar Birtaniya ga EU da ta jinkirta yarjejeniyar ficewar kasar daga ranar 29 ga watan Maris da aka sanya a baya.

Ana ganin sakamakon a matsayin nasara ga gwamnatin Birtaniya da ta gabatar da kudurin, yayin da 'yan majalisar kuma suka ki amincewa da kudurin Jam'iyyar adawa ta Labour ta sauya dabarun kasar na ficewa daga Tarayyar.(Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China