in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ta rufe taronta na shekara
2019-03-15 10:32:27 cri

 

An gudanar da taron rufe zama na 2, na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin na 13 a yau da safe, agogon birnin Beijing.

Shugaban kasar Sin, Xi Jinping da sauran shugabannin kasar ne suka halarci taron, a babban dakin taron al'ummar kasar Sin dake nan birnin Beijing

Mambobin majalisar sun amince da dokar zuba jari na bai daya ta baki na farko a kasar, wadda ta nuna yunkurin kasar na shiga wani sabon mataki na zurfafa bude kofa.

Sun kuma amince da kudure-kudure kan rahoton ayyukan gwamnati da kuma rahoton aiki na kwamitin kolin majalisar, da kotun koli na jama'ar kasar da hukumar koli mai gabatar da kararraki da gudanar da bincike ta kasar.

Baya ga haka, wakilan sun amince da rahoton tsare-tsaren tattalin arziki da na ci gaban al'umma da kuma kasafin kudin kasar da na yankuna. Har ila yau, sun amince da murabus din shugaban kwamitin kolin majalisar, Zhang Rongshun. (Fa'iza Msuatpha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China