in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan sandan Najeriya: Mutane 30 'yan bindiga suka hallaka
2019-03-06 09:25:35 cri
A kalla mutane 30 ne aka tabbatar da mutuwarsu yayin da wasu 'yan bindiga suka kaddamar da hari kan wani kauye a jihar Zamfara dake shiyyar arewa maso yammacin Najeriya, jami'an 'yan sandan yankin sun tabbatar da faruwar lamarin.

Kakakin hukumar 'yan sandan jihar ta Zamfara, Mohammed Shehu, ya fadawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa an kaddamar da harin ne kan kauyen Kware a karamar hukumar Shinkafi inda maharan suka shafe sa'o'i da dama da safiyar ranar Litinin. Maharan dai sun bude wuta ne kan jama'a mazauna kauyen sannan suka cinna wuta a gidajensu.

Daruruwa baburan hawa ne maharan suka yi amfani da su inda suka yi wa kauyen tsinke, kamar yadda wasu mazauna garin suka bayyana.

Sai dai mazauna garin sun ce adadin wadanda suka mutu ya kai 35, kana wasu mazauna kauyen da dama sun tsere daga kauyen. Sannan akwai wadanda suka bace har yanzu ba'a ji duriyarsu ba. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China