in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatan MDD a Habasha sun yi juyayin mutuwar jami'ansu 19 a hadarin jirgin saman Habasha
2019-03-12 09:47:44 cri

Jami'an MDD a kasar Habasha sun gudanar da taron girmamawa ga ma'aikatansu 19 wadanda suka mutu a sanadiyyar hadarin jirgin saman kamfanin Ethiopian Airlines na ranar Lahadi.

Taron wanda aka gudanar a babbar cibiyar taron MDD dake Addis Ababa inda aka girmama ma'aikatan MDDr 19 wadanda suka hallaka a hadarin jirgin saman samfurin Boeing 737-8 MAX a kusa da garin Bishoftu, mai tazarar kilomita 45 daga Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha a ranar Lahadi.

"Rana ce mai cike da bakin ciki," Vera Songwe, babbar sakatariyar hukuma mai kula tattalin arzikin Afrika ta MDD wato (ECA), ta bayyana hakan ne a lokacin taron zaman makokin.

Wakilan dukkanin hukumomin MDD sun hallara a kasar Habasha domin daga tuta don karrama mamatan a harabar ofishin hukumar ta ECA a jiya Litinin. (Ahamd Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China