Kamfanin jirgin sama na kasar Habasha wato Ethiopian Airlines, na shirin rubanya zirga-zirgarsa a birnin Guangzhou na kasar Sin.
Manajan Daraktan kamfanin mai kula da harkokin kasashen waje, Esayas Woldemariam, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, jirgin na shirin zuwa Guangzhou sau biyu a rana maimakon sau daya da yake zuwa.
A yanzu, jirgin na zuwa biranen Guangzhou da Beijing daga birnin Addis Ababa ne sau daya a rana, sannan ya je Chengdu sau 3 a ko wane mako.
Esayas Woldermariam, ya ce daga watan Oktoban 2019, suna shirin rubanya zirga zirgar jirginsu a Guangzhou, domin biyan bukatun fasinjojinsu dake karuwa.
Har ila yau, ya ce Kamfanin jirgin saman na shirin fara zuwa wasu karin wurare a kasar Sin, domin saukaka dangantakar dake kara kulluwa tsakanin kasashen Afrika da Sin. (Fa'iza Mustapha)