in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rufe ofishin kare hakkin dan adam na MDD a kasar Burundi cikin yanayin takaici
2019-03-06 10:23:23 cri
Kwamishiniyar hukumar kare hakkin dan adam ta MDD Michelle Bachelet ta sanar a jiya Talata cewa, "tare da nuna takaici," ofishin kare hakkin bil adama na MDD a kasar Burundi an rufe shi bayan da gwamnatin kasar ta tsakiyar Afrika ta dage kan bukatar hakan.

Kakakin ofishin kare hakkin bil adama Ravina Shamdasani ta fada a taron manema labarai cewa, an jiyo Bachelet tana cewa, "tare da nuna takaici mun riga mun rufe ofishinmu a Burundi bayan shafe shekaru 23 yana gudanar da aiki a kasar" tun daga ranar 28 ga watan Fabrairu.

Shekaru biyu ke nan tun bayan da aka dakatar da hadin gwiwa, a ranar 5 ga watan Disambar 2018, gwamnatin kasar Burundi ta bukaci a rufe ofishin kare hakkin dan adam na MDD a kasar.

Gwamnatin kasar Burundi ta ce kasar ta samu ci gaba mai yawa wajen daukar matakan bada kariya ga hakkin adam, don haka ci gaba da zaman ofishin ba shi da wata hujja. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China