in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Burundi ya yi kira da a zage damtse wajen tabbatar da nasarar samun 'yancin kai
2018-07-03 09:48:42 cri
Shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza, ya yi kira ga al'ummar kasar sa, da su zage damtse wajen yin aiki tukuru, domin tabbatar da nasarar samun 'yancin kan kasar dake gabashin Afirka.

Shugaban ya yi wannan kira ne a jiya Litinin, yayin bikin cika shekaru 56 da samun 'yancin kan kasar, wanda ya gudana a birnin Bujumbura, fadar mulkin kasar.

Manyan jagororin kasar ta Burundi ciki hadda shugaban ta Pierre Nkurunziza, da shugabannin majalissun dokokin kasar biyu, da kusoshin gwamnati, da jami'an diflomasiyya dake kasar da dama sun halarci bikin.

Kaza lika al'ummar kasar, da sassan rundunonin tsaron kasar, sun gudanar da fareti domin taya murnar wannan biki. Baya ga hakan an kuma yi wasu nune-nune domin nishadantar da al'umma.

A daya hannun kuma, shugaban kasar da manyan jami'ai, sun gudanar da karin wasu bukukuwan a wurare 2, da suka hada da ziyartar harabar ginin tunanwa da yarima Louis Rwagasore dake tsaunin Vugizo, da kuma aza furanni a filin taro na tunawa da samun 'yancin kan kasar ta Burundi. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China