in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Burundi: Dangantakar Sin da Burundi na bunkasa da kyau
2018-08-24 16:26:00 cri
Ministan harkokin wajen Burundi Alain Aime Nyamitwe ya bayyanna a kwanan baya cewa, taron koli na Beijing na FOCAC da zai gudana a watan Satumba mai zuwa, zai taimaka wajen inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, tare kuma da sa kaimi ga bunkasuwar Burundi.

Yayin zantawarsa da manema labarai a babban birnin Bujumbura ya ce, kasar na fatan kara zurfafa hadin kai da Sin a dukkanin fannoni. Sannan kasar Burundi na sa ran kara hadin kai da Sin a fannoni daban-daban, kuma tana goyon bayan taron da Sin za ta gudanar a wannan karo. A cewarsa, yayin taron kolin AU, kasashen Afrika sun bayyana kasar Sin a matsayin tsohuwar aminiya ta kwarai, wadda ta ba su taimako sosai. (Amina Xu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China