in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin Huawei na kasar Sin ya bada lambar yabo ga daliban jami'ar Zambia
2019-03-06 10:14:09 cri
Wani babban jami'in gwamnatin kasar Zambia a jiya Talata ya mika takardun shaidar lambar yabo ga wasu daliban jami'ar kasar su 3 da jami'i mai horaswa 1 a matsayin wadanda suka lashe gasar fasahar sadarwa ta zamanin ICT wanda kamfanin Huawei ya shirya a shekarar 2018/2019.

Daliban uku, wadanda suka samu nasara daga cikin dalibai 11 da suka fafata a gasar, su ne za su wakilci kasar ta Zambia a gasar ICT da aka shirya ta shiyya a kasar Afrika ta kudu daga ranar 8 zuwa 9 ga watan Maris.

Nkandu Luo, ministan ma'aikatar ilmi mai zurfi na kasar, ya yabawa kamfanin sadarwar na kasar Sin saboda shirya gasar wanda a cewarsa hakan zai taimaka wajen bunkasa cigaban fasahar sadarwa ta zamanin a kasar ta kudancin Afrika. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China