Yayin wani taron manema labarai jiya, gwamnan jihar Aminu Waziri Tambuwal, ya ce al'amarin ya auku ne a ranar Litinin da dare, a yankunan Dalijan da Rakkoni da Kalhu, wadanda ke yankin karamar hukumar Rabah na jihar.
Gwamna Tambuwal ya kuma gargadi 'yan siyasa game da furta kalamai ko yin abubuwan da za su harzuka jama'a, bayan zaben da aka kammala.
An gudanar da zaben shugaban kasa da na 'yan majalisun dokokin tarayya ne a ranar Asabar da ta gabata karkashin matakan tsaro masu tsauri a duk fadin kasar. (Fa'iza Mustapha)