in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu hare-hare sun yi sanadin mutuwar mutane 27 a Nijeriya
2019-02-27 09:45:21 cri
Wasu sabbin hare-haren da aka kai kan wasu kauyuka 4 na jihar Kaduna dake arewacin Nijeriya, sun yi sanadin mutuwar mutane 27.

Wata majiya daga rundunar 'yan sanda, ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, an samu gawarwakin mutanen ne a kauyukan da suka hada da Karamai da Gidan Gajere da Gidan Auta da kuma Chibiya, wadanda ke karkashin garin Maro, inda kuma 'yan sanda masu mukamin supeto guda 2 suka bata.

Majiyar ta ce an tura jami'an tsaro kauyukan da aka samu gawarwakin, tana mai cewa an samu galibin gawarwakin ne a kauyukan Karamai da Gidan Auta, sannan an kone gidaje sama da 40 a kauyukan.

Ta kara da cewa, daga cikin mutanen 27 har da wani dan sanda da maharan suka kashe a lokacin da yake bin sahunsu.

Cikin wata sanarwa da ta fitar a jiya, gwamnatin jihar Kaduna ta tabbatar da aukuwar lamarin, tana mai cewa jami'an tsaro na aiki domin kwantar da kura a yankin. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China