in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana fatan DPRK da Amurka za su ci gaba da tattaunawa
2019-02-28 19:25:31 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana cewa, kasarsa tana fatan kasashen Koriya ta Arewa da Amurka, za su ci gaba da tattaunawa a tsakaninsu.

Lu Kang wanda ya bayyana hakan ga taron manema labarai yayin da yake mayar da martani kan zagaye na biyu na tattaunawar kasashen biyu da ya gudana a Hanoi na kasar Vietnam, ya ce yanayin da ake ciki a zirin Koriya, shi ne babban batun da ake ta magana a kansa cikin shekarun da suka gabata. Kana batun zirin na Koriya ya sake zama wani na fage na daidaita harkokin siyasa.

A don haka ya ce, kasar Sin tana fatan Koriya ta Arewa da Amurka, za su ci gaba da tattaunawa, da nunawa juna sahihanci, da mutunta juna da martaba 'yancin juna da hada kai wajen kawar da makaman nukiliya da bullo da matakan tabbatar da zaman lafiya a zirin na Koriya. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China