in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta karyata zargin da Amurka ke mata na ganin bayan addinai a kasar
2018-12-21 21:37:54 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta karyata zargin da dan majalisar dattawan Amurka Marco Rubio ya yiwa kasarta na ganin mabiya addinin Kirsita a kasar.

Madan Hua ta bayyana hakan ne yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa. Rahotanni na cewa, a kwanakin baya ne dai Senata Rubio ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, ya damu matuka kan yadda mahukuntan kasar ta Sin ke murkushe mabiya addinin Kirista a kasar. Yana mai cewa, ana kuma tilastawa musulmai a yankin Xinjiang aikin kwadago da matsa musu lamba. Ya ce matakan kasar Sin na kawar da addini ya keta 'yancin dan-Adam

Sai dai madam Hua ta ce sanarwar da Rubio ya fitar shirme ne kawai, kuma wannan wata alama ce dake kara nuna rashin hankali wasu Amurkawa. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China