in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi watsi da zargin da mataimakin shugaban Amurka ya yi mata na tsoma baki a harkokin siyasar kasar
2018-10-05 15:43:06 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Madam Hua Chunying ta ce, kasarta ta yi watsi da zargin da mataimakin shugaban kasar Amurka Mike Pence ya yi mata game da manufofinta na cikin gida da na ketare, tana mai cewa, duk wani kazafi da Amurka ke yiwa Sin zancen banza ne.

Mataikin shugaban na Amurka yana wadancan kalamai ne yayin wani taron masu ruwa da tsaki da ya gudana a yammacin jiya Asabar, inda yake zargin cewa, wai kasar Sin na tsoma baki a harkokin cikin gida da ma na zabukan Amurkar, Sannan ya zargi kasar Sin game da manufofinta na cikin gida da na ketare.

Madam Hua ta bayyana cewa, zargin da mataimakin shugaban kasar Amurka ke yiwa kasar Sin ko kadan zancen banza ne da ba su da shaidu, sannan Amurkar ta rude game da abin da yake mai kyau da maras kyau, tana magana ne don kawai duniya ta ji ta. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China