in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun tsaron Libya sun kubutar da wasu ma'aikata yan Tunisiya 14 da aka yi garkuwa da su
2019-02-18 09:59:31 cri
A jiya Lahadi dakarun tsaron Libya sun yi nasarar kubutar da wasu ma'aikata su 14 'yan asalin kasar Tunisiya wadanda 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a kwanan baya a yammacin birnin Zawiya, mai nisan kilomita 45 daga babban birnin kasar Tripoli.

"Jami'an tsaron birnin Zawiya sun yi nasarar kubutar da ma'aikatan kasar Tunisiya. Ana ci gaba da tattaunawa da hukumomin da abin ya shafa domin tsara hanyoyin da za'a mayar da su ga iyalansu lami lafiya," inji jami'in tsaron birnin Zawiya.

Hukumar tsaron ta tabbatar da cewa ma'aikatan suna cikin koshin lafiya, kuma tuni hukumar ta wallafa hotunansu a shafinta na Facebook.

Haka zalika, ministan harkokin wajen kasar Tunisiya ya tabbatar da sakin ma'aikatan da aka yi garkuwa dasu kuma ya bayyana godiyarsa bisa kokarin da gwamnatin Libyan tayi wajen kubutar da ma'aikatan.

Da yammacin ranar Alhamis ne aka yi garkuwa da ma'aikatan a birnin Zawiya yayin da wasu 'yan binndiga suka yi awon gaba da su zuwa wani wajen da ba'a tantance ba, inji hukumar tsaron Zawiya.

Yan bindigar dai sun bukaci a saki wasu 'yan kasar Libyan da ake tsare da su a Tunisiya a matsayin musaya da ma'aikatan da suka yi garkuwa da su, kamar yadda kafafen yada labaran Tunisiyan suka ambata. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China