in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Masar ya yi taro da shugabannin kotunan koli na tsara dokokin mulki na Afirka
2019-02-20 11:06:06 cri
Shugaban kasar Masar Abdel-Fattah al-Sisi ya tattauna da shugabannin kotunan koli na tsara dokokin mulki na kasashen Afrika game da batutuwan da suka shafi ayyukan ta'addanci.

Taron, wanda aka gudanar a birnin Alkahira, ya tabo al'amurran da suka shafi rawar da hukumomin shari'a za su taka wajen yaki da rashawa da kare hakkin bil'adama, kakakin fadar shugaban kasar Masar Bassam Rady shi ne ya bayyana hakan.

Taron dai ya zo ne jim kadan bayan da kasar Masar ta karbi jagorancin kungiyar tarayyar Afrika a farkon wannan wata.

Sisi ya jaddada muhimmancin karfafa rawar da dokoki da bangaren shari'a za su taka a kasashen Afrika, wanda rashin kyautata su ke haifar da matsaloli kamar na ayyukan ta'addanci da tsattsauran ra'ayi.

Shugaban kasar Masar ya bayyana ta'addanci da cewa shi ne babban kalubale dake addabar duniya baki daya.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China