in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da cibiyar nazarin hadin gwiwar Ziri Daya da Hanya Daya a birnin Cairo
2019-01-14 09:36:08 cri

Jami'ar Renmin ta kasar Sin da jami'ar Ain Shams ta kasar Masar, a ranar Lahadi sun kaddamar da cibiyar nazarin hadin gwiwar shawarar "ziri daya da hanya daya" a Cairo, babban birnin kasar Masar.

A lokacin bikin kaddamarwar, shugaban jami'ar Ain Shams, Abdel Wahab Ezzat ya ce, an kafa cibiyar ne bayan wata yarjejeniyar da aka cimma cikin shekara guda, wanda daga bisani aka kulla yarjejeniyar fahimtar juna wanda jami'ar ta rattaba hannu, yayin da Liu Wei, shugaban jami'ar Renmin ta kasar Sin ya sanya hannu a madadin jami'arsa.

"Wannan ita ce cibiya ta biyu bayan makamanciyarta ta farko da aka kafa a kasar Rasha," in ji shi, ya kara da cewa, cibiyar za ta gudanar da nazari kan sha'anin tattalin arziki, kasuwanci da nazarin samar da kwararru, game da ayyukan hadin gwiwa tsakanin kasashen Masar da Sin.

A nasa bangaren, Liu Wei ya yaba da kafa cibiyar hadin gwiwar da jami'ar ta Ain Shams. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China