in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masar ta sake korar wani dan kasar Jamus da aka zarga da yunkurin shiga kungiyar IS
2019-01-15 11:08:42 cri
Kamfanin dillancin labaru na gabas ta tsakiya na kasar Masar, ya bayar da labari a ranar 14 ga wata cewa, kasar Masar ta sake korar wani dan kasar Jamus da aka zarga da yunkurin shiga kungiyar IS. Wannan mutum shi ne na biyu dan kasar Jamus da kasar Masar ta kora bayan zargin sa da yunkurin shiga kungiyar IS a cikin kwanaki uku.

Labarin ya bayyana cewa, wannan mutum dan shekaru 18 da haihuwa, 'yan sanda sun kama shi bayan da ya sauka daga jirgin sama daga kasar Jamus zuwa filin jiragen sama na Luxor dake kudancin kasar Masar a kwanakin baya, kuma a ranar 13 ga wata, aka kore shi daga kasar Masar.

Labarin ya bayyana cewa, 'yan sanda sun gano taswirar arewacin zirin Sinai na kasar Masar da kungiyar IS ta kan gudanar da ayyuka a jikin wannan mutum, kuma wannan mutum ya amince da yunkurinsa na shiga kungiyar IS.

Labarin ya kara da cewa, an haifi wannan mutum a kasar Masar, bayan da ya zama dan kasar Jamus, ya yi watsi da zama dan kasar Masar a shekarar 2007.

A ranar 11 ga wannan wata, gwamnatin kasar Masar ta kori wani dan kasar Jamus da aka zarga da yunkurin shiga kungiyar IS. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China